Ana Samun Tsanantar Tashe-tashen Hankula A Arewacin Kasar Mali
Dec 16, 2017 15:43 UTC
Tashar telbijin din Faransa ta 5 ta bada labarin tsanantar fadace-fadace a cikin garin Kidal da ke arewacin Mali.
rahoton ya ci gaba da cewa; Dakarun tabbatar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya da ake kira da MINUSMA, sun kutsa birnin domin gudanar da aikinsu na shimfida zaman lafiya.
Sai dai majiyar tsaro ta ce daya daga cikin dakarun na Majalisar Dinkin Duniya ya jikkata, ba tare da bayyana wanda ya kai musu harin ba.
Arewacin kasar Mali dai yana fuskantar rikice-rikice ne duk da cewa an cimma yarjejeniyar tsagaita wutar yaki a tsakanin kungiyoyin da suke dauke da makamai a yankin.
Tags