Ci Gaba Da Komawar 'Yan Gudun Hijirar Siriya Zuwa Kasarsu
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i26755-ci_gaba_da_komawar_'yan_gudun_hijirar_siriya_zuwa_kasarsu
Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da cewa: Al'ummar Siriya da suke zaune a kasar Lebanon a matsayin 'yan gudun hijira suna ci gaba da komawa kasarsu.
(last modified 2018-08-22T07:01:12+00:00 )
Dec 27, 2017 08:56 UTC
  • Ci Gaba Da Komawar 'Yan Gudun Hijirar Siriya Zuwa Kasarsu

Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da cewa: Al'ummar Siriya da suke zaune a kasar Lebanon a matsayin 'yan gudun hijira suna ci gaba da komawa kasarsu.

Kakakin Hukumar Kolin Kula da 'Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya Lisa Abou Khaled ta bayyana cewa: Dubban 'yan gudun hijirar Siriya da tashe-tashen hankula suka raba da muhallinsu kuma suka samu mafaka a cikin kasar Lebanon, suna ci gaba da komawa kasarsu, inda a halin yanzu aka kiyasta yawan mutanen da suka koma gida da cewa: Sun haura 500,000.

Lisa Abou Khaled ta kara da cewa: A watan Nuwamban da ya gabata an kiyasta cewa yawan 'yan gudun hijirar Siriya a cikin kasar Lebanon sun kai 997,905, don haka a ahalin yanzu kusan rabinsu sun koma kasarsu ta gado.