Pira Ministan Kasar Mali Ya Yi Murabus
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i26829-pira_ministan_kasar_mali_ya_yi_murabus
Ofishin shugaban kasar ta Mali ya fitar da bayani da ya kunshi cewa; Pira minista Abdullah Idrisa Maiga ya yi murabus a jiya jumaa
(last modified 2018-08-22T11:31:13+00:00 )
Dec 30, 2017 10:20 UTC
  • Pira Ministan Kasar Mali Ya Yi Murabus

Ofishin shugaban kasar ta Mali ya fitar da bayani da ya kunshi cewa; Pira minista Abdullah Idrisa Maiga ya yi murabus a jiya jumaa

Sanarwar ta kuma kara da cewa; Shugaban kasar ta Mali Ibrahim Bubakar Keita zai sanar da sunan sabon pira minista nan da wnai lokaci

Sai dai sanarwar ba ta kunshi dalilin da ya sa Pira ministan ya yi murabus din ba.

Kawo ya zuwa yanzu an kafa gwamnati hudu a karkashin shugaban kasa Ibrahim Bubakar Keita, wacce ta fara aiki tun 2013.

Kasar tana fuskantar matsalolin tsaro daga kungiyoyin da suke dauke da makamai a arewacin kasar.