An Yanke Intarnet Gabanin Zanga-zanga A Chadi
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i27603-an_yanke_intarnet_gabanin_zanga_zanga_a_chadi
Rahotanni daga Chadi na cewa an yanke hanyoyin sadarwa na intarnet a cikin daren jiya gabanin wata zanga zanga da kungiyoyin fara suka kira a kasar.
(last modified 2018-08-22T07:01:20+00:00 )
Jan 25, 2018 07:09 UTC
  • An Yanke Intarnet Gabanin Zanga-zanga A Chadi

Rahotanni daga Chadi na cewa an yanke hanyoyin sadarwa na intarnet a cikin daren jiya gabanin wata zanga zanga da kungiyoyin fara suka kira a kasar.

A yau Alhamis ne kungiyoyin fara hula a kasar suka shirya gudanar da zanga zanga nuna bacin rai dangane da hauhawar farashin man fetur da tsadar rayuwa da katse wasu kudaden alawus alawus.

An kira zanga zangar dai a kusan ilahirin lardunan kasar. 

Bayanai daga kasar na cewa an karfafa kwararen matakai na tsaro da jibge tarin jami'an tsaro a manyan tutunan N'Djamena babban birnin kasar.

An kuma rufe makarantun boko saboda halin da ake ciki.

Wannan dai na zuwa ne bayan wani yajin aiki da 'yan sufiri suka gudanar.