Congo: 'Yan Bindiga Sun Kai Wa Yankin Kivo Ta Arewa Hari
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i28305-congo_'yan_bindiga_sun_kai_wa_yankin_kivo_ta_arewa_hari
Majiyar gwamnatin kasar Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ta tabbatar da cewa masu dauke da makaman sun kai harin ne akan fararen hula a yankin Kivo ta arewa.
(last modified 2018-08-22T11:31:26+00:00 )
Feb 18, 2018 08:35 UTC
  • Congo: 'Yan Bindiga Sun Kai Wa Yankin Kivo Ta Arewa Hari

Majiyar gwamnatin kasar Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ta tabbatar da cewa masu dauke da makaman sun kai harin ne akan fararen hula a yankin Kivo ta arewa.

Kamfanin dillancin labarun Xinhua da ya nakalto labarin ya ci gaba da cewa mutane da dama ne suka rasa rayukansu yayin da wasu 8 suka jikkata.

Yankunan gabaci da arewa maso gabacin kasar ta Demokradiyyar Congo suna a matsayin sansanonin kungiyoyi masu dauke da makamai na cikin gida da kuma kasashen makwabta.

A cikin shekaru 20 da suka gabata, yankin ya zama tushen rashin zaman lafiya a kasar ta jamhuriyar Demokradiyyar Congo.

Da akwai dakarun Majalisar Dinkin Duniya wadanda suke taimakawa gwamnatin kasar domin ganin zaman lafiya ya dawo.