Najeriya : An Mika 'Yan Matan Dapchi Ga Hannun Iyayensu
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i29376-najeriya_an_mika_'yan_matan_dapchi_ga_hannun_iyayensu
Hukumomi a Najeriya sun mika 'yan matan nan na makarantar sakandaren Dapchi a hannun iyayensu a yau Lahadi.
(last modified 2018-08-22T11:31:36+00:00 )
Mar 25, 2018 18:16 UTC
  • Najeriya : An Mika 'Yan Matan Dapchi Ga Hannun Iyayensu

Hukumomi a Najeriya sun mika 'yan matan nan na makarantar sakandaren Dapchi a hannun iyayensu a yau Lahadi.

Bayanai daga yankin sun ce iyayen daliban da abokan arziki da jama'ar garin sun tarbi 'yan matan su 106 gami da namiji guda cikin murna da annashuwa.

A halin da ake ciki dai daliba guda ce mai suna Leah Sharibu, wacce Kirista ce 'yan Boko Haram din basu sako ba.

A ranar 19 ga watan Fabarairu da ya gabata ne mayakan na Boko Haram suka sace 'yan matan su 111, kafin daga bisani su sako su a ranar Laraba data gabata, amma an ce biyar daga cikin sun mutu a cikin wani yanayi da ake zaton na matsatsi ne.

Daga nan ne kuma aka garzaya da 'yan matan a fadar gwamnati dake Abuja, babban Birnin Najeriyar inda har suka gana da shugaba Muhammadu Buhari.