Kimanin Mutane 257 Suka Rasu Sanadiyar Hadarin Jirgin Soja A Aljeriya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i29818-kimanin_mutane_257_suka_rasu_sanadiyar_hadarin_jirgin_soja_a_aljeriya
Hukumomin Aljeriya sun sanar da mutuwar mutane 257 sanadiyar hadarin jirgin soja a kasar
(last modified 2019-01-16T04:00:45+00:00 )
Apr 11, 2018 06:46 UTC
  • Kimanin Mutane 257 Suka Rasu Sanadiyar Hadarin Jirgin Soja A Aljeriya

Hukumomin Aljeriya sun sanar da mutuwar mutane 257 sanadiyar hadarin jirgin soja a kasar

Cikin wata sanarwarwa da suka fitar a wannan laraba, hukumomin birnin Alge na kasar Algeriya sun bayyana cewa kimanin mutane 257 suka rasa rayukansu sanadiyar hadarin jirgin soja a kusa da filin sauka da tashi na Boufarik dake arewacin kasar, kuma yawa daga cikin wadanda hadarin ya ritsa da su, jami'an tsaro ne.

Wata majiyar tsaron kasar ta Aljeriya ta tabbatar da mutuwar dukkanin wadanda ke cikin jirgin, kuma ya zuwa yanzu ba dalilin faduwar jirgin.

Jirgin dake dauke da jami'an tsaro kimanin dari biyu, ya fadi ne jim kadan bayan tashinsa daga filin jirkin Boufarik dake kudancin kasar.