MDD Ta Damu Da Ruruwar Rikicin Tsakiyar Mali
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i32385-mdd_ta_damu_da_ruruwar_rikicin_tsakiyar_mali
Babban kwamishinan hukumar kare hakkin bil adama ta Majalsiar Dinkin Duniya, ya nuna matukar damuwarsa akan yadda rikicin kabilanci ke kara kamari a tsakiyar kasar Mali.
(last modified 2019-04-27T09:55:10+00:00 )
Jul 19, 2018 01:15 UTC
  • MDD Ta Damu Da Ruruwar Rikicin Tsakiyar Mali

Babban kwamishinan hukumar kare hakkin bil adama ta Majalsiar Dinkin Duniya, ya nuna matukar damuwarsa akan yadda rikicin kabilanci ke kara kamari a tsakiyar kasar Mali.

Da yake bayyana hakan a wani taron manema labarai a birnin Geneva, kakakin hukumar ta HCDH, Rupert Colville, ya ce abun damuwa ne halin da ake ciki a jihar Mopti dake tsakiyar kasar ta Mali, inda rikicin ya kai ga tsallake iyakokin da aka shata wa bangarorin dake rikicin.

A baya bayan dai, kwararu kan kare hakkin bil adawa dake cikin tawagar MDD a Malin, sun gano cewa fararen hula da dama a yankunan da rikicin ya shafa na kaurace wa muhallansu saboda ruruwar rikicin.

Tun farkon wannan shekara bayanan da hukumar ta fitar sun nuna cewa an samu rikicin kabilaci 99, galibi a jihar ta Mopti wadanda suka janyo hasarar rayukan fararen hula a kalla 289. 

Rikicin dai ya shafi 'yan kabilar Dogon da Bambara wadanda galibi manoma ne da kuma Fulani makiyaya.