An Kai Hari Kan Mazabu Da Dama A Mali
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i32557-an_kai_hari_kan_mazabu_da_dama_a_mali
Ma'aikatar cikin gidan kasar Mali ta sanar da cewa hare-hren da aka kai runfunan zabe da dama na kasar lamarin da ya janyo tarnaki a makomar zaben shugaban kasar.
(last modified 2018-08-22T07:02:10+00:00 )
Jul 31, 2018 02:54 UTC
  • An Kai Hari Kan Mazabu Da Dama A Mali

Ma'aikatar cikin gidan kasar Mali ta sanar da cewa hare-hren da aka kai runfunan zabe da dama na kasar lamarin da ya janyo tarnaki a makomar zaben shugaban kasar.

Kamfanin dillancin labaran Reuteus ya nakalto ma'ikatar cikin gidan Mali a jiya Litinin na cewa hare-haren da aka kai runfunar zabe da kuma rikicin da aka yi a wasu yankuna ya janyo tarnaki a makomar zaben shugaban kasar.

Ma'aikatar cikin gidan kasar ta ce kimanin runfunar zabe 644 ne aka kasa gudanar da zabe har zuwa karshe lokacin da aka tanada saboda hare-haren da 'yan bindiga suka kai.

Har ila yau ma'aikatar cikin gidan Malin ta ce kashi 3% ne kacal na runfunar zabe ne kawai aka gudanar da zabe, aka kamala ba tare da matsala ba a kasar.

Kimanin Dakarun tsaro dubu 30 ne aka tanada domin tabbatar da tsaro a yayin zaben na kasar Mali da ya gudana a ranar 29 ga watan Yuli.