An Kara Sabunta Dokar Ta Baci A Kasar Mali
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i3433-an_kara_sabunta_dokar_ta_baci_a_kasar_mali
Gwamnatin kasar Mali ta sake sabunta dokar ta baci a kasar har tsawon kwanaki 10 a nan gaba.
(last modified 2018-08-22T06:58:05+00:00 )
Apr 05, 2016 02:21 UTC
  • An Kara Sabunta Dokar Ta Baci A Kasar Mali

Gwamnatin kasar Mali ta sake sabunta dokar ta baci a kasar har tsawon kwanaki 10 a nan gaba.

A wani zaman majalisar ministoci da shugaban kasar ta Mali Ibrahim Bubakar Keita ya jagoranta a jiya abirnin Bamako, an sanar da sake sabunta dokar ta baci a fadin kasar.

Bayanin zaman ya ce har yanzu akwai sauran barazanar ta'addanci a cikin kasar da kuma wasu kasashe masu makwabtaka da kasar, kuma Mali ta dauki wannan batu da matukar muhimmanci.

Gwamnatin kasar Mali ta kafa dokar ta baci ne tun bayan kai harin da aka kai kan wani katafaren otel na Radison da ke birnin Bamako a karashen watan watan Nuwamban shekara ta 2015 da ta gabata.