CAF U20 : Nijar Da Afrika Ta Kudu Sunyi Kunnen Doki 1 - 1
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i35056-caf_u20_nijar_da_afrika_ta_kudu_sunyi_kunnen_doki_1_1
An bude gasar cin kofin Afrika ta 'yan kasa da shekara 20, wacce kasar Nijar ke karbar bakunci a bana.
(last modified 2019-02-02T17:36:50+00:00 )
Feb 02, 2019 17:36 UTC
  • CAF U20 : Nijar Da Afrika Ta Kudu Sunyi Kunnen Doki 1 - 1

An bude gasar cin kofin Afrika ta 'yan kasa da shekara 20, wacce kasar Nijar ke karbar bakunci a bana.

A karawar farko da akayi tsakanin tawagar kwallon kafa ta Nijar mai masabkin baki da ta Afrika ta Kudu, an tashi kunnen doki 1 -1 a wasan da suka guda kammala a dazu dazu.

Yanzu haka dai ana cikin karawa tsakanin tawagar kwallon kafa ta Najeriya da kuma Burundi.

Zuwa gobe Lahadi akwai karawa tsakanin Senegal da Mali, sai kuma karawa ta biyu tsakanin Burkina Faso da Ghana.