Mali : Anyi Zanga-zangar Kyammar Sojojin Ketare
Apr 19, 2016 05:29 UTC
A kasar Mali mutun guda ne aka rawaito cewa ya rasa ran sa a yayin wata zanga-zanga kyammar sojojin kasashen waje a Kidal dake arewacin kasar.
Mazauna yankin dai na adawa da ci gaba da kasancewar sojojin Faransa da na MDD dake aikin tabbatar da tsaro da yaki da ta'adanci a yankin Sahel.
Wani mazaunin Kidal ya shaidawa masu aiko da rahotanni cewa sojojin na MInusma suka bude kan masu zanga-zanga lamarin da yayi sanadin mutuwar akallah mutun guda.
Saidai tawagar ta Munusma wace ta tabbatar da zanga-zanga a cikin wata sanarwa ta ce tana ci gaba da bincike akan lamarin.
Tags