Ministan Tsaron Nijeriya: Sojojin Na Shirin Korar Boko Haram Daga Sambisa
Ministan tsaron Nijeriya Alhaji Mansur Dan'Ali ya bayyana cewar sojojin Nijeriya sun gama shirin da ake bukata wajen tarwatsa dukkanin sansanoni da maboyar 'yan kungiyar Boko Haram da suke dajin nan na Sambisa
Ministan tsaron na Nijeriya ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a wani rangadi da ya kai jihar Zamfara don gane wa idanuwansu wani wajen da ake son gina wani sabon barikicin soji a garin Gusau, babban birnin jihar inda ya ce a halin yanzu dai sojojin suna shirin shiga cikin dajin, don haka nan ba da jimawa ba za su tarwatsa 'yan ta'addan da suka buya a dajin suna ci gaba da ayyukan ta'addancin a jihohin arewa maso gabashin Nijeriyan.
Minista Dan'Ali ya kara da cewa tun bayan zuwan gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari, an samu gagaruman nasarori a kan 'yan kungiyar ta Boko, yana mai cewa suna ci gaba da aiki tare da sauran kasashen duniya wajen fada da ta'addanci a ciki da wajen Nijeriyan.
A wani labarin na daban kuma rundunar sojin kasa ta Nijeriyan, ta bakin kakakinta Kanar Sani Usman Kukasheka, ta ce ta gano wata masana'antar hada abubuwa masu fashewa na kungiyar Boko Haram a garin Ngala a jihar Borno biyo bayan wasu bayanai na sirri da suka samu inda a samamen da suka kai suka sami nasarar hallaka wasu 'yan Boko Haram din baya ga tarwatsa wajen da suka yi.