An gano tarin makamai a kan iyakakokin kasashen Mali da Aljeria
Dakarun tsaron kasar Aljeria sun gano wasu tarin makamai a kan iyakar kasar da Mali.
Ma'aikatar tsaron kasar Aljeria ta sanar da cewa a ci gaba da kokarin tsarkake iyakokin kasar daga 'yan ta'adda, Dakarun tsaron kasar sun gano runbun tsimin makamai a kan iyakar kasar da kasar Mali
Rahoton ya ce a cikin wannan runbun tsimi a kwai manya-manyan bindigogi kirar Kilashcop, bindigogin masu sarrafa kansu,tarun gurneti da kuma ababe masu fashewa.
A makun da ya gabata Ma'aikatar tsaron Aljerian ta sanar da kisan 'yan ta'adda guda 4 a yankin Auladul Hamidah.
Har ila yau a cikin wani rahoto da ta fitar na shekara, Ma'aikatar tsaron ta bayyana cewa a shekara ta 2015 Sojojin kasar sun hallaka 'yan ta'adda 157, bayan da suka kame kwamondojin su 10, da kuma makamai yaki 307.