An Halaka Yan Ta'adda 8 A Arewacin Kasar Algeria A Yau Laraba
Majiyar sojojin kasar Algeria ta bada sanarwan halaka yan ta'adda guda 8
Majiyar sojojin kasar Algeria ta bada sanarwan halaka yan ta'adda guda 8 a wani sumamen da sojojin kasar suka kai zuwa wani wuria a lardin Setf daga arewacin kasar.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto majiyar sojojin tana bayyana haka a yau Laraba ta kuma kara da cewa a jiya da daren ne sojojin suka kai sumamen a garin Kal'e zar'aa mai tazarar kilomita 280 daga babban birnin kasar, kuma cikin lardin Setif inda suka rusta da yan ta'addan suka kashe 8 daga cikinsu suka kuma gano makamai da dama a mabuyarsu.
A cikin kwanaki 10 da suka gabata majaiyar sojojin na Algeria ta bayyana cewa ta rutsa da yan ta'adda da dama a yankin gabacin kasar inda nan ma suka kashe yan ta'adda 6 suka kuma karbe makamai da dama daga hannunsu.
Tun farkon wannan shekara ne gwamnatin kasar Algeria ta kuduri anniyar ganin bayan yan ta'adda a cikin kasar.