Za A Kara Yawan Dakarun Majalisar Dinkin Duniya A Mali
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i6394-za_a_kara_yawan_dakarun_majalisar_dinkin_duniya_a_mali
Babban kwamandan dakarun majalisar dinkin duniya akasar Mali ya bayyana cewa za a kara yawan dakarun domin gudanar da ayyukan wanzar da sulhu a kasar.
(last modified 2018-08-22T06:58:24+00:00 )
Jun 07, 2016 13:37 UTC
  • Za A Kara Yawan Dakarun Majalisar Dinkin Duniya A Mali

Babban kwamandan dakarun majalisar dinkin duniya akasar Mali ya bayyana cewa za a kara yawan dakarun domin gudanar da ayyukan wanzar da sulhu a kasar.

Kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rahoton cewa, Babban kwamandan dakarun majalisar dinkin duniya a kasar Mali Mahamat Saleh Annadif ya bayayna cewa, bisa la'akari da irin barazanar da tsaro da ke ta karuwa a kasar Mali, Majalisar dinkin duniya ta amince za ta kara yawan dakarunta a kasar.

A cikin 'yan kwanakin nan dai masu da'awara jihadi suna tsananta hare-harensua yankunan arewacin kasar ta Mali, inda a baya-bayan nan suka kaddamar da hari kan sansanin dakarun na Majalisar dinkin duniya da ke yankin Gao, inda suka kashe mutane 4.