Matsanancin wuyar Ruwa a kasar Afirka ta Kudu
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i6736-matsanancin_wuyar_ruwa_a_kasar_afirka_ta_kudu
Rashin Saukar Ruwan Sama ya janyo matsanancin Wuyar Ruwa a kasar Afirka ta kudu
(last modified 2018-08-22T11:28:26+00:00 )
Jun 14, 2016 18:22 UTC
  • Matsanancin wuyar Ruwa a kasar Afirka ta Kudu

Rashin Saukar Ruwan Sama ya janyo matsanancin Wuyar Ruwa a kasar Afirka ta kudu

Rahotanni dake fitowa daga kasar Afirka ta Kudu na cewa ruwa da aka tare da manya-manyan madatsar ruwan kasar ya ragu, kuma an samu karamcin saukar ruwan sama a shekarar bara, wanda hakan shi ya janyo karamcin ruwan sha da Al'ummar kasar ke fama da shi a halin da ake ciki.

Rahoton ya ce ya zuwa yanzu Gwamnati ta kashe tsabar kudi har dalar Amurka million 32 domin kai ruwa a yankunan da ba su da ruwa a kasar.

A wata sanarwa da Gwamnatin kasar ta bayar karamcin ruwan sama ya yi sanadiyar raguwar samun albarkatun gona da kashi 14%

A nata bangare hukumar samar da abinci ta Duniya FAO ta ce farin da kasar Afirka ta kudun ta fuskanta a shekarar da ta gabata ya jefa rayuwar mutane million 16 cikin barazana, kuma a kwai yuyuwar adadin ya karu zuwa million 50.