Mali : Kungiyar Ansaruddin Ta Dauki Alhakin Kai Hari Kan Dakarun MDD
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i703-mali_kungiyar_ansaruddin_ta_dauki_alhakin_kai_hari_kan_dakarun_mdd
Harin dai na jiya Juma'a yayi sanadin mutuwar sojojin MDD da dama
(last modified 2018-08-22T06:57:48+00:00 )
Feb 13, 2016 07:49 UTC
  • wani sojin Munusma a Mali
    wani sojin Munusma a Mali

Harin dai na jiya Juma'a yayi sanadin mutuwar sojojin MDD da dama

kungiyar Ansar Dine mai kaifin kishin addini a Mali ta dauki alhakin kai hari kan dakarun MDD a arewacin kasar.

A sanarwar da kungiyar ta fitar ta hanyar kanfanin dilancin labaren Al-Akhbar na Moritaniya, kungiyar ta ce ta kai harin ne da wata mota shake da boma bobai a sansanin sojojin na Kandi dake tsakiyar Kidal, lamarin da yayi sanadin mutuwar sojojin MDD da dama tare da raunana wani adadi mai yawa a harin na jiyya Juma'a.

Sansanin dai na Kidal ya kunshi sojojin Faransa dana tawagar MDD a Mali wato Munusma.