Borkina Fasa Ta Aike Da Karin Sojoji Zuwa Kasar Mali
Jul 04, 2016 07:51 UTC
Fiye Da Sojoji Dari Takwas Ne Borkina Faso ta Aike Zuwa Kasar Mali
Kamfanin Dillancin Labarun Xinhua na kasar Sin ya ambato cewa; Kasar Borkina Faso ta aike da sojoji 850 zuwa kasar Mali.
Sojojin na Bornika Faso za su shiga karkashin dakarun majalisar dinkin duniya ce ta; (MINUSMA).
Kasashen Borkina Faso da Mali suna da iyaka mai tsawo a tsakaninsu.
A cikin watan Yuni ma kasar ta Borkina Faso ta girke Gendarme 140 a garin Gao da ke arewacin kasar Mali.
A makon da ya shude ne dai kwamitin tsaron majalisar dinkin duniya ya tsawaita lokacin aikin dakarun tabbatar da zaman lafiya a kasar Mali zuwa 2017.
Tags