Akalla Sojojin Kasar Mali 5 Ne Suka Rasa Rayukansu
A ci gaba da kaddamar da hare-hare da masu da'awar jihadi da ke da alka ada kungiyar Alkaida suke yi a Mali, wasu jami'an sojin kasar sun rasa rayukansu a wani hari da 'yan bindigar suka kai kansu.
Kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rahoton cewa, ya nakalto daga wani babban jami'in sojin kasar da ya nemi a sakaya sunansa daga birnin Bamako a yau cewa, a daren jiya wasu 'yan ta'adda na kungiyar Ansaruddin mai alaka da alkaida, sun kaddamar da wani hari kan wani sansanonin sojin kasar a yankin Mopti, inda suka kashe 5 daga cikin sojojin.
Haere-haren 'yan bindigar na kara tsananta nea kasar mali, a daidai lokacin da shugaban kasar ya kara tsawaita dokar ta faci a kasar har na tsawon watanni uku a nan gaba.
A makon da ya gabata ma wasu masu dauke da makamai sun kashe wani babban jami'in 'yan sandan kasar a yankin arewa maso yammacin kasar.