Ministan Harkokin Wajen Nijar Ya Ziyarci Iran
Nov 01, 2016 05:00 UTC
A jiya Litinin ce ministan harkokin wajen jamhuriya Nijar Ibrahim Yakuba ya gana da takwaransa na Iran, Muhammad Javad Zarif a birnin Tehran.
Ministan harkokin wajen Nijar din ya kawo ziyara ne tare da rakiyyar wata babbar tawaga data kunshi 'yan siyasa.
A yayin ziyara bangarorin biyu sun tattauna kan batutuwa da dama da suka shafi huldar a tsakaninsu.
Ibarhim Yakuba ya fadawa takwaransa cewa kasarsa a shirye take domin bude offishin jakadanci a birnin Tehran.
Shi kuwa a nasa bangare Muhammad Zarif ya yi fatan hadin gwiwa kasashen biyu wajen inganta harkokin noma, gine-gine, ma'adinai, makamashi da dai sauransu.
Tags