'Yan Takarar Shugabancin Iran Na Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe
https://parstoday.ir/ha/news/iran-i20074-'yan_takarar_shugabancin_iran_na_ci_gaba_da_yakin_neman_zabe
Dukkanin 'yan takarar neman shugabancin kasar Iran a zabe mai zuwa, suna ci gaba da yakin neman zabe.
(last modified 2019-08-10T10:24:46+00:00 )
May 04, 2017 12:21 UTC
  • 'Yan Takarar Shugabancin Iran Na Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

Dukkanin 'yan takarar neman shugabancin kasar Iran a zabe mai zuwa, suna ci gaba da yakin neman zabe.

'Yan takarar guda 6 wato Hassan Rauhani, Ishaq Jihangiri, Muhammad Baqer Qalibaf, Musatafa Agha Mir Salim, Ibrahim Ra'isi, Mustafa Hashimi Taba, a yau sun gabatar da jawabai a tashoshin talabijin daban-daban na kasar Iran.

Dukkanin bayanan nasu suna da alaka ne da irin tsare-tsaren da suke da su a fuskoki daban-daban wajen tafiyar da kasar idan suka samu nasarar lashe zabe.

A gobe ne dukkanin 'yan takarar 6 za su sake haduwa wuri guda domin tafka muhawara gaba da gaba a karo na biyu.