Kungiyar Da'ish Ta Kashe Babban Kwamandanta Abu-Hamza Al-Libiy
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i11554-kungiyar_da'ish_ta_kashe_babban_kwamandanta_abu_hamza_al_libiy
Kungiyar ta'addanci ta Da'ish ta zartar da hukuncin kisa kan daya daga cikin manyan kwamandojinta mai suna Abu-Hamza Al-Libiy da mukarrabansa 16 a garin Mosel na kasar Iraki.
(last modified 2018-08-22T06:58:59+00:00 )
Sep 25, 2016 07:49 UTC
  • Kungiyar Da'ish Ta Kashe Babban Kwamandanta Abu-Hamza Al-Libiy

Kungiyar ta'addanci ta Da'ish ta zartar da hukuncin kisa kan daya daga cikin manyan kwamandojinta mai suna Abu-Hamza Al-Libiy da mukarrabansa 16 a garin Mosel na kasar Iraki.

Tashar talabijin na Rusiyal – Yaum ta kasar Rasha ta watsa rahoton cewa: Kungiyar ta'addanci ta Da'ish ta zartar da hukuncin kisa kan daya daga cikin manyan kwamandojinta a yankin kudancin garin Mosel mai suna Abu-Hamza Al-Libiy da mukarrabansa 16 kan laifin gudu a filin yaki a lokacin da sojojin gwamnatin Iraki suka yi dirar mikiya kan yankin Al-Qadah da ke kudancin garin Mosel.

Kungiyar ta Da'ish ta kashe Abu-Hamza Al-Libiy da mukarrabansa 16 ne ta hanyar kona su da wuta a bainar jama'a a yankin Ghabat da ke garin na Mosel.

Sojojin gwamnatin Iraki da dakarun sa-kai na kasar dai sun yi nasarar 'yantar da yankin na Al-Qadah Al-Sharqat daga mamayar 'yan ta'addan Da'ish.