Syria: An gano kamfanin kera makamai A Gabacin Aleppo
Dec 07, 2016 08:29 UTC
Sojojin Syria Sun gano Kamfanin Kera Makamai
Sojojin gwamnatin Syria sun gano wani kamfanin kera makamai na 'yan ta'adda a gabacin birnin Aleppo da su ke fafatawa da su.
Kamfanin Dillancin Labarun (AFP) ya ce; kamfanin da sojojin su ka gano wanda ya ke a unguwar Hanano, ana kera makamai masu guba da kuma roka-roka a cikinsa.
Makwanni biyu da su ke gabata ne dai sojojin na Syria su ka sanar da kame unguwar Hanano daga hannun 'yan ta'adda.
Kawo ya zuwa yanzu dai sojojin na Syria suna samun nasara akan 'yan ta'adda, kuma gabacin birnin na Aleppo na gab da shiga hannun sojojin gwamnati da kawayensu.
Tags