Taron Kasashen Iran, Rasha Da Turkiyya Kan Batun Syria A Astana
Yau Litinin wakilan kasashen Rasha, Iran, da Turkiyya na taron su zagaye na biyu a birnin Astana domin tattauna yadda za'a samar zamen lafiya a kasar Syria.
Taron wanda ya hada kwararu na kuma samun halartar wakilin MDD dana kasar Jordan domin tattauna yadda za'a aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta mai daurewa a da kuma bukatar da 'yan tawayen na Syria suka gabatar a wacen taron.
Wannan dai ita ce haduwa ta biyu ta tsakanin kasashen Rasha, Iran da Turkiyya kan rikicin kasar ta Syria a Astana, bayan wace sukayi a ranakun 23 da 24 na watan Janairu daya gabata.
A wacen taron da suka gudanar bangarorin sun cimma matsaya kan batun fitar da 'yan adawa masu daukeda makamai da kuma gungun 'yan ta'adda a gabashin birnin Halep da kuma tsagaita wuta na dukkan bangarori a kasar ta Syria da rikicin shekaru shida ya daidaita.