Sojojin Iraki Na Ci Gaba Da Samun Nasara A Mosul
Feb 27, 2017 05:51 UTC
Rundinar sojin Iraki na ci gaba da samun nasara a yakin da take na neman kwato yankin Mosul daga hannun 'yan ta'addan Da'esh.
Ko a jiya Lahadi rundunar ta sanar da sake kwato yankin Mamoun dake a yammacin birnin na Mosul.
A Sanarwar da ta fitar, rundunar da ke yaki da 'yan ta'adda ta kasar ta ce ta shiga yankin na Mamoun ne wanda ke kuriyar kudu a yammacin birnin Mosul a ranar 24 ga wata,
Rundunar da ke yaki da 'yan ta'addan Iraki ta samu nasarar 'yantar da yankin Mamoun baki daya bayan wani kazamin fada da 'yan IS.
A ranar 19 ga watan nan da muke ciki ne, firaministan kasar Iraki Haider al-Abadi, ya sanar da kaddamar da matakin soja na sake kwato yammacin birnin Mosul.
Tags