Syria: Daruruwan Mayaka Sun Mika Kawukansu Ga Sojojin Gwamnati.
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i18936-syria_daruruwan_mayaka_sun_mika_kawukansu_ga_sojojin_gwamnati.
Kantoman Gundumar Homs na kasar Syria, ya ce; Fiye da mayaka 500 ne su ka mika kawukansu ga sojojin kasar tare da ajiye makamansu.
(last modified 2018-08-22T06:59:53+00:00 )
Mar 29, 2017 07:44 UTC
  • Syria: Daruruwan Mayaka Sun Mika Kawukansu Ga Sojojin Gwamnati.

Kantoman Gundumar Homs na kasar Syria, ya ce; Fiye da mayaka 500 ne su ka mika kawukansu ga sojojin kasar tare da ajiye makamansu.

Kantoman Gundumar Homs na kasar Syria, ya ce; mayaka 500 ne su ka mika kawukansu ga sojojin kasar tare da ajiye makamansu.

Talal Barazy, ya ce adadin mayakan da su ka mika kai sun kai 530, kuma za su ci gaba da rayuwarsu a matsayinsu na yan kasa.

Talal Burazi ya kuma ambaci shirin dauke masu dauke da makaman da su ka saura zuwa arewacin kasa tare da iyalansu, da hakan zai taimaka wajen samar da zaman lafiya a kasar.

A gefe daya, babban mai shari'a na gundumar Rif Damashq, Abdulmajid al-Misry ya sanar da cewa; Duk wadanda su ka ajiye makamansu a kasa, za su sami afuwar shugaban kasa.

An cimma matsaya a tsakanin gwamnatin kasar ta Syria da kungiyar 13 March, da ta ke dauke da makamai, bisa shiga tsakanin Rasha, domin fitar da su daga yankin Homs.