Siriya : Harin Bom Ya Kashe Mutum Hudu
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i20636-siriya_harin_bom_ya_kashe_mutum_hudu
Rahotonni daga Syria na cewa wani harin bom da aka kai da mota ya yi sanadin mutuwar mutane hudu tare da jikkta wasu talatin na daban a birnin Homs.
(last modified 2018-08-22T07:00:09+00:00 )
May 23, 2017 06:47 UTC
  • Siriya : Harin Bom Ya Kashe Mutum Hudu

Rahotonni daga Syria na cewa wani harin bom da aka kai da mota ya yi sanadin mutuwar mutane hudu tare da jikkta wasu talatin na daban a birnin Homs.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki biyu bayan sanarwar da sojojin gwamnatin kasar suka bayar na cewa sun kwace  daukacin ikon birnin..

Harin dai an kai shi ne a kusa da unguwar al-Zahra ta galibi musulmi yan Alawuya kabilar da shugaban kasar Bashar Al-Assad ya fito.

Unguwar al-Zahra dai ta jima tana fuskantar ire-iren wandanan hare-haren kuma mafi yawa kungiyar 'yan ta'ddan nan ta IS ce ke daukan al'hakin kaisu.