Tashin Bom Ya Lashe Rayukan Mutane 15 A Yammacin Kasar Iraki
Tashin bom a kan hanyar shigewar motoci a lardin Anbar da ke yammacin kasar Iraki ya lashe rayukan mutane akalla goma sha biyar.
Majiyar tsaron kasar Iraki ta sanar da cewa; Wani bom ya tashi a kan hanyar shigewar motoci a yankin gabashin garin Ramadi da ke lardin Anbar da ke yammacin kasar Iraki a yau Lahadi lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane akalla goma sha biyar.
A gefe guda kuma a ci gaba da samamen da jami'an tsaron Iraki da dakarun sa-kai ke gudanarwa da nufin tsarkake yankunan yammacin birnin Bagadaza fadar mulkin kasar sun yi nasarar halaka 'yan ta'adda 35 tare da jikkata wasu 19 na daban.
Har ila yau a yayin samamen jami'an tsaron Iraki sun yi nasara lalata bama-bamai kimanin 70 da 'yan ta'addan suka tanada da nufin kai hare-haren wuce gona da iri.