(ISIS) Ta Dauki Alhakin Kai Hari A Iraki
Jun 09, 2016 06:47 UTC
Rahotanni daga Iraki na cewa mutane akalla 18 ne suka rasa rayukan su, kana wasu 45 na daban suka raunana sakamakon wasu jerin hare-haren ta'adanci da kungiyar ISIS ta dauki alhakin kaiwa a Bagadaza.
Harin na farko an dai kai shi ne da wata mota a birnin Taji dake arewacin Bagadaza inda mutane a kalla bakwai suka riga gidan gaskia, kana wasu 18 suka raunana a cewar wata majiyar 'yan sanda.
Bayanai sun nuna cewa akwai jami'an tsaro da dama da harin ya rusa.
Harin na biyu kuwa an kai shi ne a daidai lokacin a wata kasuwa dake unguwar Jadida inda mutane 11 suka rasu, wasu kuma 27 suka raunana.
hare-haren kuma a cewar rahotanni sun hadasa barna mai yawa data shafi gidaje da kuma motoci.
Tags