Iraki : Dan Kunar bakin Wake Ya Kashe Mutane 7
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i8020-iraki_dan_kunar_bakin_wake_ya_kashe_mutane_7
Rahotanni daga Iraki na cewa wani dan kunar bakin wake ya kashe mutane bakwai a Bagadaza babban birnin kasar.
(last modified 2018-08-22T06:58:35+00:00 )
Jul 12, 2016 06:48 UTC
  • Iraki : Dan Kunar bakin Wake Ya Kashe Mutane 7

Rahotanni daga Iraki na cewa wani dan kunar bakin wake ya kashe mutane bakwai a Bagadaza babban birnin kasar.

Bayanai daga kasar sun ce dan kunar bakin waken da yayi jigida da boma-bamai ya tarwatsa kan sa da motar da ya ke ciki a tsakiyar kasuwar gwari dake arewa maso gabashin kasar a wannan Talata.

ko baya ga wadanda suka rasa rayukansu akwai wasu mutane 29 da suka jikkata a cewar rahotanni.

Har kawo lokacin fasara wadanan labaren babu wata kungiya data dau alhakin kai wannan harin, saidai sau tarin yawa akan danganta ire-iren wadanan ayyukan ta'adi ga kungiyar yan ta'ada mai kafirta musulmai da aka fi sani da Da'esh ko kuma (IS)