Za'a Gudanar Da Zaben Majalisar Dokokin Venezueal A Karshen Wannan Watan
https://parstoday.ir/ha/news/world-i21040-za'a_gudanar_da_zaben_majalisar_dokokin_venezueal_a_karshen_wannan_watan
Gwamnatin kasar Venezuela ta bada sanarwan cewa za'a gudanar da zaben majalisar dokokin kasar a ranar 30 ga watan yuli da muke ciki.
(last modified 2019-08-10T14:54:46+00:00 )
Jun 05, 2017 08:11 UTC
  • Za'a Gudanar Da Zaben Majalisar Dokokin Venezueal A Karshen Wannan Watan

Gwamnatin kasar Venezuela ta bada sanarwan cewa za'a gudanar da zaben majalisar dokokin kasar a ranar 30 ga watan yuli da muke ciki.

Majiyar muryar JMI daga Caracas babban birnin kasar Venezuela ta nakalto Tibisay Lucena shugaban hukumar zaben kasar yana fadar haka a jiya Lahadi, ya kuma kara da cewa kamar yadda shugaban kasar Necolas Madoro ya yi alkawari na cewa za'a gudanar da zaben majalisar dokokin kasar a baya yanzu an tsaida lokacin gudanar da wannan zaben.

Kasar Venezuela dai ta fada cikin matsalolin saiyasa mai tsanani a cikin watannin da suka gabata wanda hakan ya tialstawa shugaba Madoros daukar matati na kawo sauye saye a kundin tsarin mulkin kasar da kuma zabar sabuwar majalisar dokoki.