Iraki: "Yan ta'addar Da'esh Masu Yawa Sun Halaka A rewacin Kasar
https://parstoday.ir/ha/news/world-i21538-iraki_yan_ta'addar_da'esh_masu_yawa_sun_halaka_a_rewacin_kasar
A wani hari da jami'an tsaron kasar ta Iraki su ka kai a yankin Salahuddin, sun halaka 'yan kungiyar Da'esh 12.
(last modified 2018-08-22T11:30:17+00:00 )
Jun 21, 2017 11:57 UTC
  • Iraki:

A wani hari da jami'an tsaron kasar ta Iraki su ka kai a yankin Salahuddin, sun halaka 'yan kungiyar Da'esh 12.

A wani hari da jami'an tsaron kasar ta Iraki su ka kai a yankin Salahuddin, sun halaka 'yan kungiyar Da'esh 12.

Kantoman gundumar Salahuddin, da ake arewacin Iraki, Ahamd Abdullahi al-Jaburi, ya ce; An kai harin ne a garin al-Salam mai nisan kilo mita 15 daga arewacin Biji.

A gefe daya, babban sufeton yan sandan kasar ta Iraki, " Shakir Jaudat" ya ce; A yanzu jami'an tsaro sun killace gyauron kungiyar Da'esh a cikin tsohon birnin Mosel, sai dai yan ta'addar suna amfani da mata da kananan yara a matsayin garkuwa.