An Kashe Wani Sojin MDD A Afrika Ta Tsakiya
https://parstoday.ir/ha/news/world-i22528-an_kashe_wani_sojin_mdd_a_afrika_ta_tsakiya
Tawagar kiyaye zamen lafiya ta MDD a Afrika ta tsakiya ta sanar da mutuwar jami'inta guda da kuma raunanar wasu uku a wani harinn kauton bauna da aka kai masu a jiya Lahadi.
(last modified 2018-08-22T11:30:26+00:00 )
Jul 24, 2017 05:49 UTC
  • An Kashe Wani Sojin MDD A Afrika Ta Tsakiya

Tawagar kiyaye zamen lafiya ta MDD a Afrika ta tsakiya ta sanar da mutuwar jami'inta guda da kuma raunanar wasu uku a wani harinn kauton bauna da aka kai masu a jiya Lahadi.

A cikin sanarwar data fitar tawagar ta Munusca ta ce jami'inta da ya rasa ransa dan asalin kasar Marocco ne.

An dai kaiwa ayarin motocin jami'an harin ne a yayin da suke rakiyar motocin dake dakon ruwan sha ga al'ummar dake rayuwa a kusa da tafkin yankin. 

Tawagar dai ta dora alhakin kai harin ga mayakan Anti-Balaka ta galibi kiristoci, tare da mika ta'aziyarta ga iyalan mamacin da kuma gwamnatin ta Marocco.

Wannan dai na shi ne karon farko ba da ake kaiwa jami'an MDD hari a wannan kasa ta Arika ta tsakiya ba, inda ko a watan Mayun da ya gabata wani hari ya rusa da jami'an na MUNUSCA guda shida a kusa da iyaka da RD Congo.