Faransa : Macron Zai Ziyarci Wasu Kasashen Afrika
Shugaba Emmanuel Macron na Faransa zai fara wani ran gadi a wasu kasashen Afrika uku da suka hada da Bukina faso, Ivory Coast da kuma Ghana a wani mataki na karfafa alaka tsakanin Faransa da Afrika.
Ziyarar dai za ta maida hankali kan harkokin kasuwanci, batun matasa da ilimi da kuma makamashi da ake iya sake sarafa shi a cewar wata sanarwa daga fadar shugaban kasar.
A yayin ziyara ta sa Mista Macron zai gana da wasu matasan Afrika domin gamasar da su akan manufofin kasarsa, musamen kan kyama da wasu matasa ke yi kan barazana da suke fuskanta daga 'yan ta'adda saboda kasancewar faransa a AFrika, musamen a yankin Sahel
A Burkina faso, inda Macron zai fara yada zango a gobe Talata zai yi jawabi kan siyasar Afrika a gaban daliban jami'ar Ouagadougou su 800.
Daga bisani Macron zai halarci babban taron nahiyar AFrika da kungiyar Turai a birnin Abidjan na kasar Ivory Coast da za'a fara daga ranar 29 zuwa 30 na watan nan, kafin daga bisani ya karkare ran gadin nasa daga kasar Ghana a wani mataki na karfafa alaka da wasu kasashe da ba rainon Faransa ba.