Dakarun tsaron Jamus za su fadada aiyukansu a Mali
https://parstoday.ir/ha/news/world-i3526-dakarun_tsaron_jamus_za_su_fadada_aiyukansu_a_mali
Kasar Jamus ta ce za ta fadada aiyukan soja a Kasar Mali
(last modified 2018-08-22T06:58:05+00:00 )
Apr 07, 2016 04:02 UTC
  • Dakarun tsaron Jamus  za su fadada aiyukansu a  Mali

Kasar Jamus ta ce za ta fadada aiyukan soja a Kasar Mali

A yayin ziyarar aikin da ya kai kasar Mali jiya Laraba Ministan harakokin tsaron Jamus ya bayyana cewa kasar sa za ta kara yawan aiyukan sojan da take yi a kasar tare kuma da kara bayar da horo kan dakarunsu dake gariruwan arewacin Mali kan yadda za su tunkari 'yan tawaye masu tsaurin ra'ayi.

A Maku mai kamawa, Ministan ya ce zai a jiye wata bukata a gaban Majalisar dokokin kasar sa domin gudanar da canje-canjen da suka dace a dakarun tsaron kasar dake kasar ta Mali.

Rahoton ya ce nan gaba kasar ta jamus za ta tura Dakaru kimanin 600 a kasar ta Mali domin bayar da horo tare kuma da taimakawa kasar a yayin da ta yi da masu tayar da kayar baya.