Wajabcin Kawo Karshen Tashe-Tashen Hankula A Kasar Siriya
Wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman a kasar Siriya ya jaddada wajabcin kawo karshen duk wasu tashe-tashen hankula a kasar ta Siriya.
A zantawarsa da jaridar The Wall Street Journal ta kasar Amurka a yau Litinin; Wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman a kasar Siriya Staffan de Mistura ya jaddada cewa dole ne a kawo karshen duk wasu tashe-tashen hankula a kasar Siriya. Staffan de Mistura a yayin zaman taron birnin Munich na kasar Jamus an cimma yarjejeniyar ganin an samu wanzuwar zaman lafiya da sulhu a dukkanin yankunan kasar ta Siriya.
de Mistura ya kara da cewa: Majalisar Dinkin Duniya ba zata takaita da shirin aikewa da kayayyakin jin kai zuwa kasar Siriya ba, dole ne ta taka gagarumar rawa a fagen ganin an kawo karshen rikici da tashe-tashen hankula a kasar.
A zaman tattaunawan da ministocin harkokin wajen kasashe 15 gami da kungiyoyin kasa da kasa suka gudanar kan rikicin kasar Siriya a birnin Munich na kasar Jamus a ranar Alhamis da ta gabata sun cimma daidaiton baki kan daukan matakan kawo karshen yaki a Siriya tare da aikewa da kayayyakin jin kai zuwa yankunan kasar.