Libya: Kashe Mutane 4 A yankin Banighazi Saboda Tashin Nakiya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i10096-libya_kashe_mutane_4_a_yankin_banighazi_saboda_tashin_nakiya
Wata Nakiya da ta tarwatse a garin Banighazi da ke gabacin kasar Libya, ta kashe mutane 4.
(last modified 2018-08-22T06:58:49+00:00 )
Aug 24, 2016 07:52 UTC
  • Libya: Kashe Mutane 4 A yankin Banighazi Saboda Tashin Nakiya

Wata Nakiya da ta tarwatse a garin Banighazi da ke gabacin kasar Libya, ta kashe mutane 4.

Wata Nakiya da ta tarwatse a garin Banighazi da ke gabacin kasar Libya, ta kashe mutane 4.

Mazauna yankin  Qurashe da ke yammacin birnin Banighazi sun ce, bayan tashin nakiyar, an ci gaba da fada a tsakanin sojojin gwamnati da kuma kungiyoyin da su ke dauke da makamai a yankin.

Tsoma bakin kungiyar yarjejeniyar tsaro ta Nato a cikin kasar Libya wanda ya kai ga kashe tsohon shugaban kasar Mua''ar Khaddafi a 2011, ya share fagen tabarbarewar harkoki tsaro a kasar ta Libya.