Kamaru : Mutane 79 Suka Mutu A Hadarin Jirgi Kasa
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i12904-kamaru_mutane_79_suka_mutu_a_hadarin_jirgi_kasa
A kasar Kamaru adadin mutanen da mutu a hadarin jirgin kasa a ranar Juma'a data gabata ya kai 79.
(last modified 2018-08-22T06:59:08+00:00 )
Oct 24, 2016 12:34 UTC
  • Kamaru : Mutane 79 Suka Mutu A Hadarin Jirgi Kasa

A kasar Kamaru adadin mutanen da mutu a hadarin jirgin kasa a ranar Juma'a data gabata ya kai 79.

A wata sanarwa da aka fitar ta gidan radio na kasar wato (CRTV)  an ce adaddin ya karu ne bayan samun wasu gawarwwakin mutane 11 a jiya Lahadi.

Haka zalika a cewar sanarwar yawan mutanen da suka raunana a yayin  hadarin ya kai 551, kuma mafi yawancinsu a garzaya dasu a gidajen asibitocin gwamnatin dake Duala.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin kasar ke gudanar da zaman makoki a yau Litinin domin juyayin mutuwar mutanen da mummunan hadarin ya rusa dasu.

Hadarin dai ya auku ne ranar Juma'a data gabata a lokacin da jirgin ya kauce hanya a lardin Eseka dake tsakanin biranen Yaounde da Duala inda tazagai kimanin 11 suka jirkice.

Har kawo yanzu dai ba'a kai ga gano sanadin hadarin jirgin ba.