Nakiya Ta Hallaka Wani Sojin Faransa A Mali
Wani sojin faransa ya rasa ransa a yayin da motar da suke ciki ta taka nakiya a arewacin Mali inda gungun mayakan dake da'awar jihadi ke ci gaba da kasancewa duk da yerjejeniyar sulhun da aka cimma a shekara 2015 data gabata.
Tuni dai kungiyar Ansar Din ta Iyad Aghali dake da alaka da kungiyar 'yan ta'addan Alaida ta dauki alhakin kai harin a wata sanarwa data wallafa a shafin ta na Internet, saidai ba tare da wani karin bayyani ba, saidai cewar harin ya auku ne a nisan kilomita 60 daga birnin Kidal.
Kafin hakan wata sanarwa da ma'aikatar tsaron faransa ta fitar ta ce wasu motocin tawagar sojojin kasar a mali wato (Barkhane) sun gamu da harin wani abu mai fashewa a arewa maso gabashin Kidal.
Harin da a cewar sanarwar yayi sanadin mutuwar Marshal Fabien Jacq, tare da raunana wani sojin.
Wannan dai ya sanya adadin sojojin faransa da suka mutu a kasar ta Mali zuwa 16 tun dai lokacin da suka sanya kafa a arewacin kasar ta Mali a watan janairu na shekara 2013 da nufin yaki da masu tsatsauren ra'ayin addini.