Libya: An tseratar da Fararen Hula 14 Daga Hannun Da'esh
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i13510-libya_an_tseratar_da_fararen_hula_14_daga_hannun_da'esh
Sojojin kasar Libya Sun Kwato fararen hula daga hannun kungiyar Da'esh
(last modified 2018-08-22T06:59:12+00:00 )
Nov 07, 2016 02:58 UTC
  • Libya: An tseratar da Fararen Hula 14 Daga Hannun Da'esh

Sojojin kasar Libya Sun Kwato fararen hula daga hannun kungiyar Da'esh

Kamfanin Dillancin Labarun Reuters ya ambato cewa; Sojojin Libya sun 'yanto da fararen hula 14 bayan da su ka yi nasarar kwace wane yanki a garin sirt da ya ke a hannun kungiyar Da'esh.

Garin na Sirt  mai mutane dubu tamanin, ( 80.000) ya shiga hannun kungiyar 'yan ta'adda ta Da'esh ne a watan Aprilu na 2015. Bayan kafa gwamnatin hadin kan kasa a cikin watan Yuni na wannan shekarar da ake ciki ne dai sojojin kasar su ka fara kai farmaki da zummar kwato shi daga hannun 'yan ta'adar.

A cikin garin na Sirt, kwararrun maharban 'yan ta'adda da kuma nakiyoyi da aka dasa, suna kawo  wa sojoji cikas da hana su kwace garin cikin sauri.