Sojojin Gabacin Kasar Libya Sun Kwato Wasu Yankuna Daga Hannun Yan Ta'adda
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i14056-sojojin_gabacin_kasar_libya_sun_kwato_wasu_yankuna_daga_hannun_yan_ta'adda
Sojojin kasar Libya karkashin Janaral Khalifa Haftar sun sami nasarar kwato wasu yankuna daga hannu yan ta'adda a birnin Bengazi na gabacin kasar.
(last modified 2019-03-07T02:07:59+00:00 )
Nov 18, 2016 01:55 UTC
  • Sojojin Gabacin Kasar Libya Sun Kwato Wasu Yankuna Daga Hannun Yan Ta'adda

Sojojin kasar Libya karkashin Janaral Khalifa Haftar sun sami nasarar kwato wasu yankuna daga hannu yan ta'adda a birnin Bengazi na gabacin kasar.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya bayyana cewa majiyar watsa labarin ta sojojin Kalifa Haftar ne suka bayyana wannan labarin a jiya Alhamis, sannan labarin ya kara da cewa a halin yanzu umguwar Alkawasha na birnin Bengazi ta koma karkashin ikon sojojin sannan a fafatawarsu da yan ta'addan a jiya dun rasa sojoji 18 a yayinda wasu 54 suka ji rauni.

Labarin ya kara da cewa sojojinsu 4 ne suka rasa rayukansu sanadiyyar tashin bom a kan hanyarsu a yankin. Unguwar Alkawasha dai daya ne daga cikin sansanonin kungiyar Daesh a birnin na Bengazi, kuma yana da tazarar kilomiya goma daga tsakiyar birnin. 

A ranar Laraba ma, wata majiyar ta fadawa Reuters cewa a fafatawar sojojin Haftar da yan ta'adda a birnin na Bengazi sojoji 20 ne suka rasa rayukansu a yayanda wasu 40 suka ji rauni. 

Tun fiye da shekaru biyu da suka gabata yan ta'adda ta kunkiyar Daesh suke fafatawa da sojojin Khalifa Haftar a birnin na Bengazi.