Libya: Halifa Haftar Ya Ki Yin Sulhu Da Gwamnatin Hadin Kan Kasa.
Kwamandan sojojin kasar ta Libya a gabacin kasar ya yi watsi da duk wani yunkurin sulhu da gwamnatin hadin kan kasa.
Kwamandan sojojin kasar ta Libya a gabacin kasar ya yi watsi da duk wani yunkurin sulhu da gwamnatin hadin kan kasa.
Halifa Haftar ya ce; Shekaru biyu da su ka gabata an yi tattaunawa da Fa'iz Suraj wanda shi ne Pira ministan gwamnatin hadin kan kasa a yanzu, amma babu wani sakamako da ya haifar, kuma har yanzu kasar babu abinda ya sauya.
Haftar ya kara da cewa a halin da ake ciki a yanzu, mayakansa ne su ke rike da kaso 80% na kasar ta Libya.
Bangarorin da su ke da sabani da juna a kasar Libya sun bude tattaunawa a kasar Aljeriya domin fahimtar juna da kawo karshen rikicin kasar.