An Gano Gawakin Yan Ta'adda Fiye Da 100 A Arewacin Kasar Libya
Majiyar sojojin kasar Libya ta bayyana cewa an gano daruruwan gawakin yayan kungiyar Daesh a birnin Sirt wanda aka kwace daga hannunsu a yan makonnin da suka gabata.
Kakakin sojojin kasar ta Libya Mohammad Al_gasri ne ya bayyana haka a jiya Laraba ya kuma klara da cewa tun lokacinda aka kwace birnin daga hannunu a cikin yan makonninn da suka gabata an gano gawakinsu kimani 2500 sannan har yanzun akwai zaton cewa wasu daruruwan suna bisne karkashin tarkashen gine ginen da aka rusa a kansu.
Al-gasri ya kammala da cewa babu wani dan kungiyar Daesh wadanda suka yi iko da birnin da ya fice zuwa waje, sai dai akwai yayan wannan kungiyar a kudancin kasar wanda zai dauki shekaru kafin a kawo karshen su a yankin .