Faduwar Jirgin Sama Na Yaki A Gabacin Kasar Libya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i18960-faduwar_jirgin_sama_na_yaki_a_gabacin_kasar_libya
Wani jirgin sama na yaki, ya fado a gabacin kasar Libya, bayan kai wa sansanonin 'yan ta'adda hari.
(last modified 2018-08-22T06:59:53+00:00 )
Mar 30, 2017 06:40 UTC
  • Faduwar Jirgin Sama Na Yaki A Gabacin Kasar Libya

Wani jirgin sama na yaki, ya fado a gabacin kasar Libya, bayan kai wa sansanonin 'yan ta'adda hari.

Wani jirgin sama na yaki,  ya fado a gabacin kasar Libya, bayan kai wa sansanonin 'yan ta'adda hari.

Kamfanin Dillancin Labarun Faransa ya nakalto cewa; Jirgin yakin Samfurin Mig 21 ya fado kasa bayan wani hari da ya kai wa sansonin 'yan ta'adda a garin Dhubrukh da ke gabacin kasar ta Libya. Matukin jirgin wanda ya ke karkashin Halifa Haftar ya mutu.

Libya dai ta fada cikin matsalolin tsaro da yaki a tsakanin kungiyoyi daban-daban tun bayan faduwar Mu'ammar Khaddafi a 2011.

Wasu kungiyoyin 'yan ta'adda a kasar sun sami iko da rijiyoyin man fetur da kasar ta ke da shi.