Aljeriya Ta Jaddada Bukatar Warware Rikicin Kasar Libiya Ta Hanyar Lumana
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i19852-aljeriya_ta_jaddada_bukatar_warware_rikicin_kasar_libiya_ta_hanyar_lumana
Minista mai wakiltan gwamnatin Aljeriya a kungiyar tarayyar Afrika da na hadin kan kasashen Larabawa ya jaddada bukatar daukan matakin warware rikicin kasar Libiya ta hanyar lumana.
(last modified 2018-08-22T07:00:01+00:00 )
Apr 27, 2017 01:19 UTC
  • Aljeriya Ta Jaddada Bukatar Warware Rikicin Kasar Libiya Ta Hanyar Lumana

Minista mai wakiltan gwamnatin Aljeriya a kungiyar tarayyar Afrika da na hadin kan kasashen Larabawa ya jaddada bukatar daukan matakin warware rikicin kasar Libiya ta hanyar lumana.

Abdul-Qadir Musahil ya jaddada cewa; Kawo karshen matsalolin tashe-tashen hankula da nufin wanzar da zaman lafiya da sulhu a Libiya yana bukatar gudanar da zaman taron kasa tsakanin dukkanin bangarorin siyasar kasar.

Musahil ya kara da cewa: Matsayin gwamnatin Aljeriya a kungiyar tarayyar Afrika da na hadin kan kasashen Larabawa shi ne kokarin ganin an warware rikicin kasar ta Libiya ta hanyar lumana musamman kasancewar Aljeriya a matsayin makobciyar kasar ta Libiya.  

Abdul-Qadir ya kuma jaddada daukan kwararan matakai a fagen yaki da kungiyoyin 'yan ta'adda da nufin wanzar da zaman lafiya a dukkanin nahiyar Afrika dama duniya baki daya.