Sojojin Aljeriya Sun Gudanar Da Atisayi A Kan Iyaka Da Kasar Libya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i19892-sojojin_aljeriya_sun_gudanar_da_atisayi_a_kan_iyaka_da_kasar_libya
Sojojin gwamnatin kasar Aljeriya sun gudanar da wani gagarumin atisayi a yankin Amnas da ke kan iyakan kasar da kuma kasar Libya.
(last modified 2018-08-22T07:00:02+00:00 )
Apr 28, 2017 12:27 UTC
  • Sojojin Aljeriya Sun Gudanar Da Atisayi A Kan Iyaka Da Kasar Libya

Sojojin gwamnatin kasar Aljeriya sun gudanar da wani gagarumin atisayi a yankin Amnas da ke kan iyakan kasar da kuma kasar Libya.

Kamfanin dillancin labaran Anatoli ya habarta cewa, dakarun kasar Aljeriya sun sanar da kammala babban atisayin da suka gudanar a kan iyakokin kasarsu da kuma Libya, da nufin kara zama cikin shirin ko ta kwana domin murkushe 'yan ta'addan takfiriyyah da ke barazana ga tsaron kasar.

Mahukuntan kasar Aljeriya sun ce tun bayan faduwar gwamnati a Libya, kasar ta Aljeriya take fuskantar babbar barazana ta tsaro daga 'yan ta'adda da suka tarua  cikin kasar Libya daga kasashen duniya daban-daban, wanda hakan yasa ala tilas a dauki kwararn matakan tsaro a kan iyakokin kasashen biyu.