Wani Bom Ya Tarwatse A Birnin Mogadishu Fadar Mulkin Kasar Somaliya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i19928-wani_bom_ya_tarwatse_a_birnin_mogadishu_fadar_mulkin_kasar_somaliya
Majiyar tsaron Somaliya ta sanar da cewa: Wani bom ya tarwatse a birnin Mogadishu fadar mulkin kasar Somaliya, inda ya jikkata wasu mutane biyu.
(last modified 2018-08-22T11:30:02+00:00 )
Apr 29, 2017 17:44 UTC
  • Wani Bom Ya Tarwatse A Birnin Mogadishu Fadar Mulkin Kasar Somaliya

Majiyar tsaron Somaliya ta sanar da cewa: Wani bom ya tarwatse a birnin Mogadishu fadar mulkin kasar Somaliya, inda ya jikkata wasu mutane biyu.

Majiyar tsaron Somaliya ta sanar da cewa wani bom ya tarwatse a kusa da motar wani dan Majalisar Dokokin kasar a birnin Mogadishu fadar mulkin kasar a yau Asabar, inda ya jikkata wasu mutane biyu.

Majiyar ta kara da cewa: babu wata kungiya da ta dauki alhakin tada bom din, sai dai kungiyar ta'addanci ta Al-shahab ita ce ta yi kaurin suna a fagen kaddamar da hare-haren wuce gona da iri kan al'ummar Somaliya.

Magajin garin birnin Mogadishu Yusuf Jamal ya yi furuci da cewa an samu sauki kai hare-haren wuce gona da iri a birnin na Mogadishu amma duk da haka jami'an tsaron kasar suna ci gaba da gudanar da sintiri da nufin kalubalantar duk wata barazana ta mayakan kungiyar ta'addanci ta Al-Shabab.