Libya: Hari A Wani Barikin Soja Ya Kashe Mutane 141
A jiya da dare ne kakakin sojan kasar Libya Ahmad al-Mismari ya ce; An kai hari akan sansanin soja a garin Burak wanda ya ci rayukan abinda bai gaza mutane 141 ba.
A jiya da dare ne kakakin sojan kasar Libya Ahmad al-Mismari ya ce; An kai hari akan sansanin soja a garin Burak wanda ya ci rayukan abinda bai gaza mutane 141 ba.
Ahmad al-mismari ya zargi kungiyar da ta ke dauke da makamai agarin Misarata da kai hari.
Mafi yawancin sojojin da aka kashe din wadanda su ke a karkashin Halifa Haftar ne da ke iko da yankuna da dama na gabacin kasar.
Harin ya zo ne bayan da aka sami fahimtar juna a tsakanin Halifa Haftar da kuma pira ministan gwamnatin hadin kan kasa,. Faez al-Siraj.
Libya, tana fama da matsalolin tsaro tun 2011 da aka kifar da gwamnatin Mu'ammar Khaddafi.