An Kaiwa Sojojin Mali Hari
Wasu 'Yan bindiga sun kai hari Sansanin Sojin kasar Mali dake arewacin kasar , lamarin da yayi sanadiyar mutuwar Sojoji biyar tare da jikkata wasu takwas na daban
Rahotanni dake fitowa daga kasar Mali sun habarta cewa a safiyar jjiya Assabar wasu 'yan bindiga da ba akai ga gane ko su waye ba sun kai harin kan Dakarun tsaron kasar a barikinsu na garin Bintagoungou dake arewacin kasar., lamarin da yayi sanadiyar mutuwar Sojoji 5 tare da jikkata wasu 8 na daban
Rahoton ya ce an kai harin ne da misalin karfe biyar na asubahin jiya Asabar, kuma maharan sun lalata illahirin kayan aikin sojojin gwamnatin da ke a cikin wannan barikin soja da ke a nisan kilomita 80 da birnin Tombouctou daya daga cikin manyan biranen yankin Arewacin kasar.
Wasu shaidun gani da ido a garin na Bintagoungou sun ce maharan sun kwashi ganimar kayan yaki mai yawa kana sun kama wasu sojojin sun tafi da su.